Browsing Category
Labarai
Labaran karshe da sabbin abubuwan dake faruwa a Najeriya da ma duniya baki daya.
Majalisar Shari’a Ta Musulunci Ta Ƙaryata Labarin Kiran Addu’ar Cire Shugaban INEC
Majalisar ƙoli ta Shari’a a Najeriya (SCSN) ta ƙaryata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa ta buƙaci Musulmi su yi addu’ar cire shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan.
A wata sanarwa da ta fitar a Kaduna ranar!-->!-->!-->…
Osimhen Zai Ƙarawa Gaban Barcelona Matuƙar Ƙarfi In Ji Yamal
Matashin ɗan wasan Barcelona, Lamine Yamal, ya buƙaci shugabannin kulob ɗin su fifita ɗaukar ɗan wasan gaba na Najeriya, Victor Osimhen, kafin kakar wasa mai zuwa.
Rahoton jaridar Fichajes ya bayyana cewa Yamal na kallon Osimhen a!-->!-->!-->…
Bayan Fuskantar Zazzafar Tattaunawa da Al Jazeera, Bwala Ya Ce An Yi Masa Tiyata a Maƙogwaro
Mai ba Shugaban Najeriya shawara kan sadarwa, Daniel Bwala, ya bayyana cewa ya yi tiyatar maƙogwaro kwanaki takwas bayan wata tattaunawa mai zafi da ɗan jarida Mehdi Hasan na Al Jazeera.
Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da tashar!-->!-->!-->…
Rikicin Gabas Ta Tsakiya: Najeriya Zata Samu Maƙudan Kuɗaɗe Yayinda Japan Zata Sayi Ɗanyen Manta da…
Ƙasashen duniya na ci gaba da fuskantar tangarɗar samar da makamashi yayin da ƙasar Japan ta fara tuntuɓar masu samar da ɗanyen mai, ciki har da Najeriya, domin tabbatar da wadataccen mai a cikin gida.
Rahoton kamfanin dillancin labarai!-->!-->!-->…
INEC Ta Ɗage Sabunta Rijistar Masu Kaɗa Ƙuri’a a Najeriya Har Sai Bayan Zaɓen 2027
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta sanar da ɗage aikin sake tantance rajistar masu kaɗa ƙuri’a a faɗin kasar har sai bayan babban zaɓen 2027.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Juma’a, wadda!-->!-->!-->…
TUC Ta Buƙaci Dawo Da Bayar Da Tallafin Man Fetur Ga Matatun Mai na Najeriya
Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƴan Kasuwa a Najeriya (TUC) ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta yi amfani da kuɗaɗen ƙarin kuɗin shiga na mai domin tallafawa matatun mai na cikin gida su rage raɗaɗin hauhawar farashin fetur ga ƴan kasa.
Shugaban!-->!-->!-->…
Yanda Rashin Wutar Lantarki Ya Ci Gaba da Jefa Ƴan Najeriya cikin Duhu Duk da Alƙawurran Gwamnati
Rahoton da jaridar BusinessDay ta wallafa na musamman ya nuna yadda matsalar wutar lantarki a Najeriya ke ci gaba da ta’azzara duk da alƙawurran da gwamnatin tarayya ta ɗauka tun daga shekarar 2023.
Lokacin da Ministan Wutar Lantarki,!-->!-->!-->…
Janar na Soji da Wasu Sojoji Sun Rasa Rayukansu a Sabbin Hare-Haren Ƴan Ta’adda a Borno
Wani babban jami’in sojin Najeriya mai muƙamin Brigediya Janar da wasu sojoji sun rasa rayukansu sakamakon sabbin hare-haren ƴan ta’adda a wasu yankunan Jihar Borno.
Hare-haren sun faru ne a wurare huɗu daban-daban a daren Laraba, inda!-->!-->!-->…
Ɓarayin Kayan Sadarwa Sun Yi Kaka-Gida da Hasumiyoyin Sadarwa a Najeriya, Suna Jawo Asarar Miliyoyin…
Wasu ƙungiyoyi masu aikata laifuka sun mayar da hasumiyoyin sadarwa a Najeriya tamkar wuraren da akai musu ajiya don ɗiba, inda suka sace muhimman kayayyakin lantarki guda 656 a jihohi 14 a shekarar 2025 kaɗai, kamar yadda rahoton Hukumar!-->…
Iran Ta Fitar da Sabbin Hanyoyi a Mashigin Hormuz Don Kare Jiragen Ruwa Daga Faɗawa Haɗari
Iran ta sanar da sabbin hanyoyin zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz, tana mai gargaɗin cewa babbar hanyar na iya kasancewa cikin haɗari sakamakon yiwuwar bi ta kan nakiyoyi a ruwa.
Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da!-->!-->!-->…