Browsing Category
Manyan Labarai
Labaran da suka fi muhimmanci a kasa da duniya.
TUC Ta Buƙaci Dawo Da Bayar Da Tallafin Man Fetur Ga Matatun Mai na Najeriya
Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƴan Kasuwa a Najeriya (TUC) ta buƙaci gwamnatin tarayya da ta yi amfani da kuɗaɗen ƙarin kuɗin shiga na mai domin tallafawa matatun mai na cikin gida su rage raɗaɗin hauhawar farashin fetur ga ƴan kasa.
Shugaban!-->!-->!-->…
Janar na Soji da Wasu Sojoji Sun Rasa Rayukansu a Sabbin Hare-Haren Ƴan Ta’adda a Borno
Wani babban jami’in sojin Najeriya mai muƙamin Brigediya Janar da wasu sojoji sun rasa rayukansu sakamakon sabbin hare-haren ƴan ta’adda a wasu yankunan Jihar Borno.
Hare-haren sun faru ne a wurare huɗu daban-daban a daren Laraba, inda!-->!-->!-->…
Ɓarayin Kayan Sadarwa Sun Yi Kaka-Gida da Hasumiyoyin Sadarwa a Najeriya, Suna Jawo Asarar Miliyoyin…
Wasu ƙungiyoyi masu aikata laifuka sun mayar da hasumiyoyin sadarwa a Najeriya tamkar wuraren da akai musu ajiya don ɗiba, inda suka sace muhimman kayayyakin lantarki guda 656 a jihohi 14 a shekarar 2025 kaɗai, kamar yadda rahoton Hukumar!-->…
Iran Ta Fitar da Sabbin Hanyoyi a Mashigin Hormuz Don Kare Jiragen Ruwa Daga Faɗawa Haɗari
Iran ta sanar da sabbin hanyoyin zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz, tana mai gargaɗin cewa babbar hanyar na iya kasancewa cikin haɗari sakamakon yiwuwar bi ta kan nakiyoyi a ruwa.
Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da!-->!-->!-->…
Wasu Ƙungiyoyi Sun Buƙaci Goodluck Jonathan Ya Tsaya Takarar Shugaban Ƙasa a 2027
Wata gamayyar ƙungiyoyi daga jihohi 36 da Abuja ta buƙaci tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, da ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027.
Shugaban ƙungiyar, Tom Ohikere ne ya bayyana hakan a wani gangami da aka yi a Abuja.
Ya ce!-->!-->!-->!-->!-->…
PDP Ɓangaren Wike Ya Yi Watsi da Taron ADC da Wasu Jiga-Jigan Jam’iyyar
Ɓangaren jam’iyyar PDP da ke ƙarƙashin jagorancin Nyesom Wike ya buƙaci mambobinsa da su yi watsi da wani taro da ɓangaren Taminu Turaki ya yi da jam’iyyar ADC.
Kakakin ɓangaren na ƙasa, Jungudo Mohammed, ya ce taron ba shi da izini!-->!-->!-->…
Tattaunawar Iran da Amurka Na Fuskantar Barazana Saboda Rikicin Lebanon
Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya bayyana cewa hare-haren da ake kaiwa Lebanon da sauran saɓani sun kawo cikas ga tattaunawar tsagaita wuta da Amurka.
Ya ce yarjejeniyar da ake dogaro da ita ta riga ta rushe,!-->!-->!-->…
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasarta Kan Zuwa Najeriya Saboda Tsanantar Matsalar Tsaro
Gwamnatin Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasarta da su guji tafiya Najeriya tare da umartar ma’aikatanta masu sauƙin aiki su fice daga ƙasar, watanni biyar bayan ayyana Najeriya a matsayin “Country of Particular Concern.”
A wata sanarwa da!-->!-->!-->…
Majalisar Zamfara Ta Dakatar da Shugabannin Ƙananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahana
Majalisar dokokin Jihar Zamfara ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomi biyu bisa zargin karkatar da kuɗaɗe da kuma ƙin bada bayanai kan yadda aka kashe su.
Waɗanda abin ya shafa sun hada da Mannir Mu’azu Haidara na Kaura Namoda da!-->!-->!-->…
Jigawa Ta Yi Fice Yayinda INEC Ta Yi Rajistar Sabbin Masu Zaɓe Kusan Miliyan 3 da Rabi a Najeriya
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa a Najeriya (INEC) ta sanar da cewa ta yi rajistar sabbin masu zaɓe sama da miliyan 3.4 a mataki na biyu na shirin rajistar masu zaɓe da ake yi a faɗin ƙasar.
A cewar rahoton mako na 13 da aka fitar a!-->!-->!-->…