The news is by your side.

Abin da hukuncin da Kotun Ƙoli ta yi kan shugabancin PDP da ADC ke nufi da matakan da jam’iyyun ke ɗauka

95

Kotun Ƙoli ta Najeriya a ranar Alhamis, 30 ga Afrilu, 2026 ta yanke hukunce-hukunce biyu masu muhimmanci da suka sauya yanayin rikicin shugabanci a jam’iyyun adawa na Peoples Democratic Party (PDP) da African Democratic Congress (ADC).

Kotun ta soke babban taron jam’iyyar PDP da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025, tare da dawo da tsarin shugabancin ADC ƙarƙashin tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark.

A cikin hukuncin da Mai shari’a Mohammed Garba ya yanke, kotun ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa, tare da tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin sakatare na ƙasa.

Rikicin ADC ya samo asali ne bayan ƙarar da aka shigar domin hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) amincewa da shugabancin Mark da Aregbesola har sai an kammala shari’ar.

Mai shari’a Garba ya bayyana cewa kotun farko ba ta amince ko ta ƙi bayar da umarnin hana wani abu ba, illa dai ta bayar da umarni na wucin gadi domin kiyaye halin da ake ciki.

Ya ce rashin neman izinin kotu kafin ɗaukaka ƙara ya sanya ƙarar ba ta da inganci a doka, yana mai jaddada cewa “ingancin takardar ɗaukaka ƙara yana da nasaba da hurumin kotu.”

Kotun ta kuma soke umarnin “status quo ante bellum”, tana mai cewa irin wannan umarni na wucin gadi ne kawai domin hana canja halin da ake ciki yayin da shari’a ke gudana.

A martaninsa, sakataren yaɗa labarai na ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hukuncin a matsayin tabbacin sahihancin shugabancin jam’iyyar.

Ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, “wannan hukunci ya tabbatar da cewa shugabancin jam’iyyar ƙarƙashin Sanata David Mark da Ogbeni Rauf Aregbesola sahihi ne kuma bisa doka yake.”

Shi ma mai neman takarar shugaban ƙasa a ADC, Mohammed Hayatu-Deen, ya ce hukuncin ya nuna muhimmancin bin doka da oda a tafiyar demokaraɗiyyar Najeriya.

Sai dai duk da haka, ADC ta buƙaci shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya yi murabus, tana mai zargin cewa matakin cire amincewa da shugabancin Mark ya nuna ɗaukar ɓangare.

A ɓangaren PDP kuwa, kotun ƙolin ta soke taron jam’iyyar na Ibadan saboda an gudanar da shi duk da umarnin kotu da ke hana hakan.

A hukuncin da Mai shari’a Stephen Adah ya jagoranta a ƙara mai lamba SC/CV/164/2026, kotun ta ce masu ɗaukaka ƙara sun karya dokar kotu a fili.

Ya ce, “rashin bin umarnin kotu ba abin da ake jayayya a kai ba ne,” yana mai cewa hakan barazana ce ga tsarin shari’a a Najeriya.

Kotun ta kuma zargi ɓangaren da Taminu Turaki (SAN) ke jagoranta da neman umarni daga wata kotu daban domin kauce wa hukuncin da ke kansu.

Mai shari’a Adah ya bayyana hakan a matsayin “babban cin zarafin tsarin shari’a” da ke barazana ga demokaraɗiyya.

Kotun ta jaddada cewa jam’iyyun siyasa dole ne su bi dokokin ƙasa da kuma umarnin kotuna, kamar yadda sassa na 221, 222 da 229 na kundin tsarin mulki na 1999 suka tanada.

Bayan hukuncin, wasu manyan jiga-jigan PDP ciki har da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, da na Jihar Bauchi, Bala Mohammed, sun gudanar da taron gaggawa a Abuja domin tattauna makomar jam’iyyar.

Rahotanni sun ce taron ya gudana ne a Bauchi House da ke Asokoro, Abuja, tare da halartar mambobin kwamitin amintattu (BoT), majalisar zartarwa ta ƙasa da sauran shugabanni.

Shugaban kwamitin amintattu na PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya sanar cewa BoT ta karɓi ragamar shugabancin jam’iyyar na wucin gadi yanzu.

Ya bayyana a cikin sanarwar cewa, wannan mataki ya zama dole domin cike giɓin shugabanci bayan hukuncin Kotun Ƙoli.

Wabara ya ƙara da cewa dukkan matakan da aka ɗauka ƙarƙashin wasu shugabannin da aka dakatar yanzu sun zama marasa inganci a doka.

Sai dai ɓangaren da ke da alaƙa da Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce hukuncin ya tabbatar da sahihancin shugabancin Abdulrahman Mohammed a jam’iyyar ne.

Mai magana da yawun ɓangaren, Jungudo Mohammed, ya ce “hukuncin kotun ƙoli ya kawo ƙarshen rikicin ɓangaranci a PDP.”

Amma wani ɓangare ƙarƙashin jagorancin Seyi Makinde ya ce jam’iyyar yanzu ba ta da sahihin shugabanci, yana mai cewa dole ne hukumomin jam’iyyar su ɗauki matakin gyara al’amura.

Rikicin cikin gida ya raba PDP zuwa ɓangarori biyu, yayin da ADC ma ta samu rabuwar kai zuwa ɓangarori uku daban-daban.

Masu sa ido na ganin cewa waɗannan hukunce-hukuncen na Kotun Ƙoli za su yi tasiri sosai ga siyasar jam’iyyun adawa gabanin zaɓen shekarar 2027 a Najeriya.