The news is by your side.

INEC ta kammala mataki na biyu na rajistar masu zaɓe da mutum miliyan 3.7

75

Hukumar Independent National Electoral Commission (INEC) ta sanar da kammala mataki na biyu na ci gaba da rajistar masu zaɓe (CVR) a ranar Juma’a 17 ga Afrilu 2026, inda aka samu rajista 3,748,704 a faɗin Najeriya.

Darakta mai kula da wayar da kan masu zaɓe da hulɗa da jama’a, Victoria Eta-Messi ce ta bayyana hakan a rahoton mako na 14 da aka fitar a Abuja.

Ta ce adadin ya haɗa da mutum 2,259,288 da suka yi rajista ta yanar gizo da kuma 1,489,416 da suka kammala rajistar su a cibiyoyi daban-daban.

A cewarta, waɗannan alkaluma na wucin gadi ne kuma za a ci gaba da tantance su domin tabbatar da ingancinsu.

Ta ƙara da cewa bayan kammala rajistar, hukumar za ta fara nuna rijistar masu zaɓe domin karɓar ƙorafe-ƙorafe da gyara bayanai.

Za a gudanar da wannan aikin daga ranar 29 ga Afrilu zuwa 5 ga Mayu 2026 a cibiyoyi da aka tanada a faɗin ƙasar.

Victoria Eta-Messi ta buƙaci duk waɗanda suka yi rajista su je su tabbatar da sahihancin bayanansu tare da bayar da rahoton duk wata matsala.

Ta ce hakan zai taimaka wajen gano rajistar da aka maimaita, sunayen waɗanda suka rasu da kuma waɗanda ba ƴan ƙasa ba.

Hukumar ta bayyana cewa an gudanar da mataki na farko daga 18 ga Agusta 2025 zuwa 10 ga Disamba 2025, yayin da na biyu ya gudana daga 5 ga Janairu zuwa 27 ga Afrilu 2026.

Ta kuma ce za a sanar da ranar fara mataki na uku nan gaba.

A ƙarshe, ta jaddada cewa INEC na da niyyar tabbatar da rijistar masu zaɓe mai tsafta da sahihanci domin gudanar da zaɓe nagari.