The news is by your side.

El-Rufai Ya Ce Zai Halarci Babban Taron ADC Yayin da Shari’arsa ke Gudana

49

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa zai halarci babban taron jam’iyyar ADC “a zuciyarsa” yayin da yake fuskantar shari’a.

Ya bayyana hakan ne bayan fitowarsa daga kotun Jihar Kaduna ranar Litinin.

El-Rufai, wanda aka tsare fiye da wata guda, ya isa kotu da misalin karfe 9 na safe domin ci gaba da shari’ar da ake yi masa kan tuhume-tuhume guda tara daga hukumar ICPC.

Bayan zaman kotun na kusan awanni huɗu, ya fito tare da lauyoyinsa.

Da aka tambaye shi kan taron ADC, ya ce, “Zan halarta, amma a zuciyata,” daga nan aka tafi da shi cikin mota Hilux ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro.

Ana zarginsa da laifukan cin zarafin ofis, damfara da nuna gata ba bisa ƙa’ida ba tare da wani mutum mai suna Amadu Sule.

A wajen kotun an ga jami’an tsaro da dama ciki har da ƴan sanda da DSS.

Lamarin na janyo hankalin jama’a sosai, musamman ganin irin tasirin da El-Rufai ke da shi a siyasar Najeriya.

Ana sa ran shari’ar za ta ci gaba a kwanaki masu zuwa.