The news is by your side.

Masana a Majalisar Ɗinkin Duniya sun soki hare-haren Isra’ila a Lebanon, sun nemi dakatar da sayar mata da makamai

42

Gungun masana a Majalisar Ɗinkin Duniya sun bayyana hare-haren Isra’ila a Lebanon a matsayin na haramun, suna kira ga ƙasashe mambobi da su dakatar da tura makamai zuwa Isra’ila.

Masanan 19 da ke aiki a fannoni daban-daban na haƙƙin ɗan adam sun fitar da sanarwar ne a ranar Laraba yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare a kudancin Lebanon da suka kashe aƙalla mutane 16, ciki har da ma’aikatan jinya huɗu, a cewar rahotannin Lebanon.

Sun ce harin ba kariyar kai ba ne, suna bayyana shi a matsayin keta dokokin Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma barazana ga zaman lafiya da tsarin ƙasa da ƙasa.

Sun kuma yi kira ga Isra’ila da ta dakatar da dukkan ayyukan soji a Lebanon, tare da neman dakatar da tura makamai idan aka samu hujjar take haƙƙin ɗan adam.

Rahotanni sun nuna cewa tun daga watan Maris Isra’ila ta ƙara kai hare-hare a Lebanon, lamarin da ya jawo mutuwar mutane sama da 2,000 tare da raba fiye da miliyan 1.2 da muhallansu.

Masanan sun ce tilasta wa jama’a ƙaura na iya zama laifin cin zarafin bil’adama, suna kuma zargin an lalata gidaje a wasu yankuna da ke da rinjayen mazhabar Shi’a.

Isra’ila ta ce tana kai hare-hare ne kan ƙungiyar Hezbollah, yayin da aka samu rahotannin tattaunawar tsagaita wuta da ke gudana tsakanin ɓangarorin.