Ƙasashen Oman da Iran sun gudanar da ganawar mataimakan ministocin harkokin wajensu domin tattauna hanyoyin tabbatar da zirga-zirgar jiragen ruwa cikin sauƙi a mashigin Hormuz.
A cewar Al Jazeera, an gudanar da taron ne tare da ƙwararru daga ɓangarorin biyu.
Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen Oman ta ce an tattauna hanyoyi daban-daban na tabbatar da zirga-zirga duk da halin da yankin ke ciki.
Rahotanni sun nuna cewa wasu jiragen Oman uku sun ratsa mashigin a wani yanayi na daban, kusa da gaɓar ƙasar Oman.
Wannan na zuwa ne yayin da Iran ke taƙaita zirga-zirga tun bayan yaƙin da Amurka da Isra’ila suka fara a kanta.
Mashigin Hormuz na da matuƙar muhimmanci ga safarar mai da iskar gas zuwa Turai da Asiya.
Masana sun ce duk wani rikici a yankin na iya jefa kasuwar makamashi ta duniya cikin tashin hankali.
Wani masani, Amin Saikal, ya gargaɗi cewa faɗaɗa rikicin “zai jefa yankin cikin bala’i”, yana mai kira ga sasanci.
A halin yanzu, ana ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya domin warware matsalar.